Kamfanin dillancin labaran iqna, ya bayar da rahoto dangane dad akin ajiye kayan tarihin muslunci na kasar malayzia, wanda ya hada abubuwa da dama da suka shafi tarihi na addinin muslucni, kama daga kwafin littafai da kur’anai, da kuma abubuwa na karau masu tsohon tarihi.
Kur’anin Iran wani kur’ani ne na tarihi, wanda asalinsa daga yankin arewacin Afrika ya fito a cikin shekara ta 1622, daga nan kuma zuwa Hijaz Saudiyya ta yanzu, haka nan kuma a lokacin mulkin Salujikawa ya shiga hannunsu, bayan wani lokaci kuma an tafi da shi zuwa gabashin nahiyar asiya, inda a halin yanzu yakea kasar ta Malaysia ana kula da shi.
Tandis Taghavi, wata mai ilimin kula da kayan tarihi ce wadda ta halarci baje kolin kayan tarihi na mlaysia daga birnin manila na kasar Phllipines.