IQNA

Azhar Ta Nuna Damuwa Kan Karuwar Matsalolin Tsaro A Najeriya

22:41 - June 02, 2021
Lambar Labari: 3485976
Tehran (IQNA) Cibiyar da ke sanya ido kan lamurran musulmi a duniya da ke karkashin Azhar ta nuna damuwa kan karuwar matsalolin tsaro a Najeriya.

A wani rahoto da shafin yada labaraiu na Alwafd ya bayar,  cibiyar da ke sanya ido kan lamurran musulmi a duniya da ke karkashin cibiyar Azhar da ke Masar ta sanar da cewa, bisa ga rahotanni da hukumomin tsaro suke fitarwa a Najeriya, a cikin lokutan baya-bayan nan satar mutane tare da yin garkuwa da su yana kara kamari a kasar.

Bayanin ya ci gaba da cewa, mafi muni a cikin lamarin shi ne yadda masu aikata wannan mummunan laifin suke sace yara ‘yan makaranta tare da yin garkuwa da su da cutar da su, wanda hakan yana sanya fargaba matuka dangane da makomar lamurran tsaro a Najeriya, wanda tabbas zai cutar da harkar ilimi a kasar.

Haka nan kuma bayanin cibiyar ya yi ishara da cewa, wajibi ne day a rataya kan hukumomin Najeriya  su kara zage dantse su yi kamar suna yi, domin ganin sun tunkari wannan mummunan aiki da bata gari suke yia  kasar, haka nan kuma su kara matsa kaimi wajen tunkarar yaduwar ta’addanci da sunan addini ko jihadi a kasar.

 

3975103

 

 

captcha