Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, kamfanin dillancin labaran Anatoli ya bayar da rahoton cewa, Salihovic shi ne limamin masallaci musulmi a garin Novi Pazar, wanda ya sha duka da zagi da cin zarafi daga wasu mutane.
Gamayyar kungiyoyin musulmi a kasar Serbia ta fitar da bayani da ke cewa, sakamakon duka da aka yi wa malamin, ya samu munanan raunuka a jikinsa.
Jami'an tsaro sun ce har yanzu ba su kame kowa kan lamarin ba, amma dai suna gudanar da bincike domin sanin wadanda suke da hannu wajen aikata wannan aika-aika.
Wannan dai ba shi ne karon farko da musulmi suke fuskantar irin wannan cin zarafi a kasar Serbia ba, kuma lamarin yana kara ta'azzara ne a cikin shekarun baya-bayan nan, sakamakon bullar kungiyoyi masu adawa da musulmi a kasar.